Wani matashi wanda ya bayyana kaunar da yake yiwa jarumar Kannywood, Maryam Yahaya a fili ya ce ba zai iya rayuwa a duniya ba idan jarumar bata raye.
Da haka ne yace yana fatan Ubangiji ya dauki rayuwarsa a ranar da zai dauki rayuwar jarumar.
A wani bidiyo na TikTok da matashin yayi wanda shafin Kannywood celebrities ya wallafa, an ga matashin yana bayyana sirrin da ke ransa.
Ya fara ne da cewa:
“Hakika, gaskya ni bazan iya rayuwa babu Maryam Yahaya ba, ba wai kuma ina nufin a karkashin inuwata ba.
“Ba zan iya rayuwa ba muddin bana jin motsinta, ko da a birnin kif take. Shiyasa a ko da yaushe nake addu’a, duk ranar da Allah ya tashi daukar ran jaruma Maryam Yahaya, to ya dauka tare da nawa.
“Saboda idan babu Maryam
Babu abinda yake sa ni bakin ciki kamar in na tuna zan mutu in tarar da Allah, Jaruma Maryama Yahaya
Fitacciyar jarumar Kannywood, Maryam Yahaya yayin zantawa da BBC Hausa ya shaida cewa babu abinda ya fi bakanta mata rai kamar ta tuna cewa watarana zata mutu ta tarar da Allah.
Idan ba a manta ba, a shekarar da ta gabata ne jarumar ta yi wani gagarumin ciwo wanda yasa ta fita daga hayyacin ta har wasu suka dinga tunanin mutuwa zata yi.
Ciwon ya yi matukar sauya mata halitta har ta kai ga wadanda suka san ta basa gane ta, yanzu haka dai ta warke sarai tamkar bata taba ciwo ba.
A ranar Alhamis, 17 ga watan Maris a wani bidiyo wanda BBC Hausa ta wallafa na tattaunawar da aka yi da ita ta bayar da takaitaccen tarihin ta.
Kamar yadda tace:
“Ni dai sunana Maryam Yahaya, an haife ni a garin Kano, Anguwar Goron Dutse.”
Ta ci gaba da cewa ta yi karatun firamare da sakandare, sannan tun tana karama ta ke sha’awar fara fim wanda yanzu haka take gode wa Allah akan fim din da ta ke yi.
Ta ce ta fara fim a shekarar 2016 wanda ta fara da fim
din ‘Masur’ kuma a yanzu haka bata san yawan fina-finan da ta yi ba kuma duk tana son su sosai.
Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayinku a wajen sharhi dake kasa.
Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:
Leave a Reply