Yanzu-yanzu: Wata Tsawa Mai Karfin Gaske Ta Fadon ma Maryam ‘Yar Dan Majalisan Tarayya Da Wani Dan Agaji a Jihar Jigawa da Katsina:

Tsawa Ta Fadowa Wata Yarinya A Makarantar Islamiyya A JiharJigawa da Wani Dan Agaji A Katsina

 Hon Saleh Shehu Hadejia cewar wata tsawa mai karfi ta fadowa wata yarinya mai suna Maryam Rabiu Garba Kaugama a garin Kaugama dake jihar Jigawa.

Marigayiyar ‘ya ce ga tsohon dan majalistar taraiyya mai wakiltar Malammadiri da Kaugama.

Lamarin ya faru ne a lokacin da ta je cikin makarantar Islamiyya domin yin karatun Alqur’ani Mai Girma.

Allah Ubangiji ya gafarta mata.

Wata Tsawar Ta Kashe Dan Agaji Duk A Yau:

A wani bangaren kuma wani wakilin namu ya ruwaito daga Nura Rabe Dandagoro cewar wata Tsawar kuma Ta Yi Silar Mutuwar Dan Agaji Addinin Musulunci A Jihar Katsina

“Sakamakon ruwan da aka tafka hade da tsawa ta yi sanadiyyar rasuwar makwabcinmu mai suna Attahiru Abdu, wanda kafin rasuwarsa yana aikin Agaji na Fityanul Islam”.